Connect with us

News

Kotu ta yi watsi da bukatar bayar da belin Abba Kyari

Published

on

Daga Muhammad Muhammad zahraddin

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta ƙi amincewa da buƙatar bayar da beli da dakataccen mataimakin kwamishinan ‘yan sanda Abba Kyari yake nema.

Advertisement

Mai shari’a Emeka Nwite ne ya ƙi amincewa da bukatar ba da belin yayin yanke hukunci kan bukatar a yau Litinin.

An gurfanar da Abba Kyari da wasu mutum shida a gaban kotu bisa zargin safarar hodar iblis.

Advertisement

Mai shari’an, Emeka Nwite ya bayyana cewa hujjoji da hukumar Hana sha da fatucin miyagun kwayoyi NDLEA ta gabatar mata sun kai ta ki bada belin Abba Kyarin da wasu mutum shida.

Hukumar ta NDLEA da take kawo hujjojin neman yin fatali da bukatar neman beli da Abba kyari ya yi, ta ce ta yi la’akari da ƙwaƙƙwarar shaida da yanayin da ke tattare da zargin da ake masa, bai kamata kotun ta bayar da belinsa ba.

Advertisement

NDLEA ta fada wa kotun kuma cewa yanayin lafiyar Abba Kyari abu ne wanda za ta iya kula da shi da kuma bai fi karfinta ba, wanda kuma hakan yasa kotun taki amincewa da bukatar beli da Abba Kyari yake nema a gabanta.

Idan za a iya tunawa dai, Ana zargin Abba Kyari da wasu ‘yan sanda shida da hannu a safarar hodar iblis.

Advertisement

Ana kuma zargin Kyari da karɓar cin hanci a hannun matashi ɗan Najeriya kuma mazaunin Amurka mai suna Ramon Abbas, wanda aka fi sani da Hushpuppy, Sai dai ya musanta zarge-zargen.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending