Connect with us

News

2023: Duk jihar da rikicin siyasa ya tashi laifin gwamnoni ne  – Mathew Kukah

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Babban Limamin Ɗariƙar Cocin Katolika na Sokoto, Mathew Kukah, ya yi kira ga ‘yan Najeriya cewa su ɗora laifin ɓarkewar rikice-rikicen siyasa a kan gwamnonin jihohi.

 

Advertisement

Ya ce akasari duk rikicin siyasar da ya tashi da wanda zai tashi kafin nan da zaɓen 2023, duk gwamnonin jihohi ne musabbabin su.

Jami’ar ABU, da Birtaniya sun amince tare da gudanar da bincike kan yaran da ba sa zuwa makaranta a Najeriya da Pakistan da Tanzaniya.

Kukah ya yi wannan tsokaci a cikin wata hira da gidan talabijin na Arise TV ya yi da shi a ranar Talata.

Advertisement

 

Ya ce wasu gwamnonin jihohi ƙiri-ƙiri su na hana jam’iyyun siyasa yin amfani wuraren taruka mallakar jihohi, lamarin da faston ya ce hakan na haifar da rikicin siyasa a jihohi daban-daban.

Advertisement

 

Wannan bayani na Kukah ya zo kwanaki huɗu bayan Mashawarcin Shugaba Muhammadu Buhari kan tsaro, Babagana Monguno ya bayyana cewa a cikin kwanaki 30 bayan fara kamfen, an samu tashe-tashen hankula a wurare 52 cikin jihohi 22.

Advertisement

 

“Ni ina ganin cewa gwamnoni sun fi sauran rukunan ‘yan Najeriya laifin haddasa ɓarkewar tashe-tashen hankula. Saboda su ne masu wuƙa da naman da ke riƙe da wasu wuraren da dalilin su rikicin ke yawan tashi,” inji Kukah.

Advertisement

 

Ya ce sannan kuma wasu gwamnonin da su ka canja sheƙa zuwa wata jam’iyyar na haddasa rikici ta hanyar ƙoƙarin tirsasa wa sauran jami’an gwamnati bin su zuwa jam”iyyar da su gwamnonin su ka koma.

Advertisement

 

“Kuma abin takaici ne yadda waɗannan gwamnoni ke nuna kamar ba su da masaniyar cewa magoya bayan su na kekketa fastar jam’iyyun adawa.”

Advertisement

 

Ya ce abin damuwa ne matuƙa yadda waɗannan gwamnoni ba su ɗaukar darasi daga kura-kuren da su ka tafka a baya, wanda ya yi sanadiyyar ɓarkewar tarzomar siyasa.

Advertisement

 

Da ya ke bada misalin halayyar ‘yan siyasa da wani bidiyon da aka nuno Atiku Abubakar da Bola Tinubu zaune a filin jirgi su na raha da annashuwa, Kukah ya ce hakan darasi ne da ya kamata talaka ya ɗauka cewa su fa ‘yan siyasa duk ‘dodo ɗaya su ke wa tsafi’, wato dukkan su abokan juna ne masu tseren rige-rigen kaiwa ga dukiyar al’umma kawai.

Advertisement

 

A kan haka sai ya ja hankalin jama’a cewa su guji nuna wa ‘yan siyasa makauniyar soyayya, domin duk yadda ‘yan siyasa ke gaba ko adawa, wata rana tare za ka gan su, wuri ɗaya kuma a jam’iyya ɗaya.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending