Connect with us

News

Sabon Kwamishinan Yan Sandan Kano Ya Kama Aiki.

Published

on

 

Sabon kwamishinan rundunar yan sandan jihar Kano CP Muhammad Yakubu ya kama aiki, bayan dauke tsohon kwamishina, Mamman Dauda, zuwa jihar Plateau domin gudanar da zaben 2023.

Advertisement

 

Mai magana da yawun rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da ya fitar a Talatar nan.

Advertisement

Gwamnoni uku sun kai ƙarar Emefiele da Malami kan raina kotu

Sanarwar tace rundunar ta tura, CP Ita Uko-Udom, a matsayin wanda zai kula da shiyar Kano ta tsakiya a zaben, sai kuma DCP Adamu Isa Ngoji da DCP Abdulkadir El-Jamil za su kula da shiyar kudancin Kano yayin da DCP Abaniwomda S.Olufemi zai kula da shiyyar Kano ta Arewa don kula da harkokin zaben.

 

Advertisement

Kiyawa yace sabon kwamishinan ya tabbatar wa al’ummar Kano cewa za a yi zabe mai tsafta.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending