News
Tinubu ya miƙa wa Majalisar Dattawa sunayen ministoci
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Tsohon gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike, ya shiga cikin jerin sunayen ministocin da aka karanta a zauren majalisar dattawa da yammacin ranar Alhamis da shugaban kasa Bola Tinubu
Tsohon gwamnan jihar Ebonyi, Dave Umahi; da mai magana da yawun shugaban kasa, Dele Alake shi ma ya sanya jerin sunayen.
Tinubu Ya Roki Kungiyar Kwadago Ta NLC Data Dakatar Da Shirinta Na Tafiya Yajin Aiki.
Bayan dogon jiran da ‘yan Najeriya suka yi, shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Femi Gbajabiamila, a ranar Alhamis, ya gabatar da jerin sunayen ministocin Tinubu a gaban majalisar dattawa.
Gbajabiamila, wanda shi ne tsohon kakakin majalisar wakilai, ya gabatar da jerin sunayen ga shugaban majalisar dattawa Godswill Akpabio da misalin karfe 01:19 na rana.
Daga nan ne Akpabio ya karanta jerin sunayen ministoci tare da sunayen mutane 28.
Abubakar Momoh
Yusuf Maitama Tukur
Ahmad Dangiwa
Hannatu Musawa
Uche Nnaji
Betta Edu
Dr. Diris Anite Uzoka
Dauda Umahi
Ezenwo Nyesom Wike
Muhammad Badaru Abubakar
Nasiru El Rufa’i
Ekerikpe Ekp[o
Nkiru Onyejiocha
Olubunmi –
Stella Okotete
Uju Kenedy Ohaneye
Bello Muhammad Goronyo
Dele Alake
Lateef Fagbemi
Mohammed Idris
Olawale Edun
Waheed Adebanwp
Emman Suleman Ibrahim
Prof Ali Pate
Farfesa Joseph Usev
Abubakar Kyari
John Enoh
Sani Abubakar Danladi
