Connect with us

News

Ƙungiyoyin Ma’aikatan Jami’o’i sun sanar da tsunduma yajin aiki a faɗin Najeriya

Published

on

Ƙungiyoyin Ma’aikatan Jami’o’i sun sanar da tsunduma yajin aiki a faɗin Najeriya

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI

Ƙungiyoyin Ma’aikatan Jami’o’in Najeriya ta tsunduma yajin aikin sai-baba-ta-gani saboda rashin biyan ‘ya’yanta albashinsu na watanni huɗu a shekarar 2022.

Advertisement

Kwamitin haɗin guiwa na ƙungiyoyin ma’aikatan jami’o’in (JAC) a ƙarkashin jagorancin shugaban ƙungiyar ma’aikata ta SSANU, Mohammed Ibrahim, da Sakatare-janar ƙungiyar NASU Peters Adeyemi, ne suka tabbatar da ɗaukar wannan mataki a cikin wata sanarwa suka sanya wa hannu.

Zaɓen Kananan Hukumomi: Kungiyoyin Farar Hula 89 Sun Gabatar Da Rahoto Ga  Hukumar KANSIEC 

Ƙungiyoyin biyu sun ce za su fara wannan yajin aiki ne daga ranar Litinin 28 ga watan October a matsayin wani mataki na nuna halin ko-in-kula da gwamnatin tarayya take yi game da albashinsu na watanni huɗu da aka rike musu tun 2022.

Advertisement

Sakamakon haka, ƙungiyoyin suke umartar dukkan ‘ya’yansu da ke jami’o’i da sauran cibiyoyi da ke da alaƙa da su tsunduma yajin aikin kuma ka da su ba da ƙofa kowacce irin na tattaunawa da kowa.

 

Advertisement

PREMIUM TIMES

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending