Connect with us

News

Rundunar ƴan sandan ta kori wasu jami’anta 

Published

on

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta sanar da daukar mataki ladabtarwa kan harbe-harben da ya faru a ranar 26 ga watan Afrilun bana a garin Effurung na jihar Delta, wanda ya kai ga mutuwar wani Mr Mene Ogidi.

Wannan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in yaɗa labaran rundunar ƴan sandan DCP Anthony Okon Placid ya fitar yau Laraba.

Advertisement

Hukumomin sun yanke hukuncin cewa jami’in ɗan sanda ASP Nuhu Usman ya aikata laifukan da suka saɓa da dokokin tsaro, da sauran sharuɗan amfani da makami.

A don haka, rundunar ƴan sanda ta kori ASP Nuhu Usman da sauran jami’an da aka kama da laifin aikata harbi ba bisa ƙa’ida ba.

Advertisement

Haka zalika, rundunar da za ta miƙa mutanen da suka aikata laifin zuwa ga hukumomin shari’a da ke da hurumin yanke musu hukunci.

 

Advertisement

RFI

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending