Connect with us

News

Hisbah ta kama mutane 31 kan zargin karuwanci da shan barasa

Published

on

HISBAH

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Dakarun Hukumar Hisbah a jihar Jigawa sun kama mutane 31 da su ka haɗa da mata 25 a Ƙaramar Hukumar Kazaure da ke jihar a yau Laraba, bisa zargin su da laifin aikata munanan dabi’u.

Advertisement

Kwamandan Hisbah a jihar, Ibrahim Dahiru, ya ce an kama wadanda ake zargin ne da misalin karfe 6 na safe bisa zargin karuwanci da shan barasa.

Sojoji sun kama tabar wiwi ta N4.9m a Yobe

Advertisement

Ya shaida wa manema labarai a Dutse a yau Laraba cewa, an kama wadanda ake zargin ne a wani samame da hukumar Hisbah ta kai mai taken: “Abin da ka shuka shi za ka girba”.

Kwamandan ya ce an kama kwalabe 55 na barasa iri-iri da kuma lita 50 na Burukutu’ a yayin farmakin.

Advertisement

Ya ce an mika wadanda ake zargin da kayayyakin da aka kama ga ‘yan sanda a yankin domin ci gaba da daukar mataki.

Mista Dahiru ya yabawa mazauna jihar bisa goyon bayan da suke baiwa hukumar Hisbah wajen gudanar da ayyukanta.

Advertisement

Ya kuma bayar da tabbacin cewa Hisbah za ta ci gaba da yaki da munanan dabi’u a duk sassan jihar.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending