Connect with us

News

Maciji Ya Shiga Wandon Bature ‎

Published

on

3023

Wani ɗan yawon buɗe ido ɗan ƙasar Jamus mai shekaru 57 ya rasu bayan da maciji ya cije shi a yayin da yake kallon wasan masu sarrafa macizai a wani otel da ke birnin Hurghada na ƙasar Masar.

‎A cewar jami’an ‘yan sandan Jamus, lamarin ya faru ne a farkon watan nan, lokacin da mutumin ke hutu tare da iyalansa a bakin Tekun Bahar Maliya.

Advertisement

Gobara Ta Kone Filaza A Kano 

‎Rahotanni sun ce wasan, wanda ke cikin shirye-shiryen nishaɗin otel ɗin, ya ƙunshi macizai guda biyu da ake zargin nau’in cobra ne, inda mai wasan ke rataye su a wuyan masu kallo domin burge su.

Advertisement

‎Sai dai hatsarin ya auku ne lokacin da ɗaya daga cikin macizan ya kutsa cikin wandon mutumin, inda ya cije shi a ƙafarsa.

‎Jami’an tsaro sun ce mutumin ya nuna alamun guba mai tsanani bayan cizon, inda aka yi masa taimakon gaggawa kafin a kai shi asibiti.

Advertisement

‎Sai dai daga bisani ya rasu duk da ƙoƙarin ceton rayuwarsa.

‎Hukumomi a Jamus sun ce sun fara gudanar da bincike kan yadda lamarin ya faru, yayin da ake jiran sakamakon gwaje-gwajen sinadaran guba domin gano cikakken bayani kan mutuwar.

Advertisement

‎A cewar Hukumar Lafiya ta Duniya, dubban mutane na rasa rayukansu a kowace shekara sakamakon cizon maciji a faɗin duniya.

 

Advertisement

CNN

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending