Connect with us

Politics

Taron Kano Ya Tabbatar Da Cewa Tinubu Ba Shi Da Wani Abin Da Zai Tsinanawa Yan Najeriya – Atiku

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

 

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP Atiku Abubakar, ya ce ganin yadda Tinubu ya gaza yin wata magana mai daukar hankali gaban jama’a a jihar Kano, ya nuna ba zai yi wa ‘yan Nijeriya abin kirki idan ya gaji shugaba Buhari ba.

Advertisement

 

A cikin wata sanarwa da mai Magana da yawun sa Phrank Shaibu ya fitar, Atiku Abubakar ya bayyana haka ne bayan Tinubu ya tara jama’a a Kano yayin gangamin yakin neman zaben sa.

Advertisement

 

Rahotanni sun ce, bayan an kashe makudan kudade wajen shirya taron gangamin a Kano, Tinubu ya kasa fadin wata magana mai ma’ana a wajen taron.

Advertisement

 

Sanarwar ta cigaba da cewa, maimakon Tinubu ya yi magana mai ma’ana, sai ya rika tikar rawa a bainar nasi wanda hakan ya tabbatar babu abinda zai iya tsinanawa yan Najeriya a cewar sanarwar.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending