News
JAMB Ta Saki Sakamakon Ɗalibai Miliyan 1.9
Hukumar shirya jarrabawar shiga manyan makarantu ta ƙasa (JAMB) ta sanar da fitar da ƙarin sakamakon jarrabawar UTME ta shekarar 2026, yayin da ake ci gaba da gudanar da jarrabawar a faɗin Najeriya.
A wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar, Fabian Benjamin, ya fitar, ya ce sabon sakamakon ya shafi ɗaliban da suka rubuta jarrabawar a ranakun 17 da 18 ga watan Afrilu.
An Haramta Wa ‘Yan Kabilar Igbo Nadin Sarautar Gargajiya A Kasashen Waje
Sanarwar ta bayyana cewa an fitar da sakamakon ɗalibai 1,264,940 daga cikin waɗanda suka rubuta jarrabawar a ranakun biyu, kuma an buɗe damar duba sakamakon nan take.
Hukumar ta ce ɗalibai za su iya duba sakamakonsu ta hanyar aika saƙon “UTMERESULT” zuwa lambobin 55019 ko 66019, ta amfani da layin wayar da suka yi rajista da shi.
Tun da farko, JAMB ta fitar da sakamakon ɗalibai 632,752 da suka rubuta jarrabawar a ranar 16 ga watan Afrilu.
Da wannan sabon saki, jimillar sakamakon da aka riga aka fitar ya kai 1,897,692.
Ana gudanar da jarrabawar UTME ne a matakai daban-daban a cibiyoyi daban-daban a faɗin ƙasar, kuma hukumar ta ce za ta ci gaba da sakin sauran sakamakon a hankali yayin da ake kammala jarrabawar.
Fiye da ɗalibai miliyan 2.2 ne suka yi rajista domin rubuta jarrabawar ta bana, adadin da ke nuna ƙaruwar masu neman shiga manyan makarantu idan aka kwatanta da shekarar da ta gabata.
An fara gudanar da jarrabawar ne a ranar 16 ga watan Afrilu, kuma ana ci gaba da ita a wurare daban-daban a sassan Najeriya.
