Connect with us

News

Shugaban Tinubu Zai Gana Da Ƙungiyoyin Ƙwadago Kan Mafi Ƙarancin Albashi

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

Za a sake yin zama tsakanin Shuagaba Bola Ahmed Tinubu da ƙungiyoyin kwadago kan batun mafi karancin albashi ga ma’aikata.

Advertisement

Jaridar ‘Tribune’, ta ruwaito cewa wani babban jami’in NLC ya ce Tinubu ya gayyaci wakilan ƙungiyoyin zuwa fadar shugaban ƙasa da ke Abuja domin tattaunawar.

Sanata Kawu Sumaila Ya Shigar Da Kuduri Domin A Raba Jihar Kano Gida 2 

A ranar Alhamis ne za a gudanar da zaman inda ƙungiyoyin NLC da TUC suna kan bakansu na cewa 250,000 suke buƙatar ya zama sabon mafi ƙarancin albashi ga ma’aikatan.

Advertisement

A kwanakin baya ne gwamnatin tarayya ta ce Naira 62,000 kawai za ta iya biya inda ake fatan a zaman a samu maslaha a tsakanin ɓangarorin biyu da za a yi a gobe Alhamis

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending