Connect with us

News

Ba Mu Fara Daukar Sabbin Ma’aikata Ba  — Shugaban Hukumar KAROTA 

Published

on

Kotu Ta Ja Kunnen Jami,an  KAROTA Akan Yanda Suke Gudanar Da Aikinsu

DAGA MAIMUNATU BASHIR MUSA 

Hukumar Kula da Zirga zirgar Ababen Hawa ta jiha KAROTA ta musanta jita-jitar da ake yadawa na fara daukar aiki a Hukumar

Advertisement

Shugaban Hukumar KAROTA Engr. Faisal Mahmud Kabir ne ya bayyana haka a jiya, ta bakin mai magana da yawon Hukumar Nabilusi Abubakar Kofar Na’isa

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Cewa ‘Yan Najeriya Su Shirya Karin Kudin Wutar Lantarki 

Ya ce Hukumar ta Kula da jita-jitar da ake yadawa na fara daukar sabbin Jami’an Hukumar wadanda hakan ba gaskiya ba ne

Advertisement

Sai dai ya ce Hukumar na tsaka da aikin tantance daukacin Jami’an KAROTA domin duba yuwuwar daukar sabbin Jami’an

A don haka Hukumar ke gargaðin jama’a, da su guji yada jita-jitar fara daukar sabbin Jami’an KAROTAR

Advertisement

Hukumar ta ce duk wanda ta kama da hannu wajen yada jita-jitar zata gurfanar da shi gaban sharia domin ya girbi abinda ya shuka

Engr. Faisal ya roki jama’a da su yi gaggawar sanar da Hukumar ta KAROTA ko ofishin Yansanda mafi kusa wanda duk aka samu yana yada jita-jitar

Advertisement

A karshe Hukumar ta ce idan za a dauki sabbin Jami’an za a sanar a Hukumance ta kafafen yada labarai

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending