News
Rundunar ‘Yan Sanda Ta Kori jami’anta Da Ya Kashe Wani Matashi A Delta
Rundunar ƴan sandan Najeriya ta sanar da daukar mataki ladabtarwa kan harbe-harben da ya faru a ranar 26 ga watan Afrilun bana a garin Effurung na jihar Delta, wanda ya kai ga mutuwar wani Mr Mene Ogidi.
Wannan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in yaɗa labaran rundunar ƴan sandan DCP Anthony Okon Placid ya fitar yau Laraba.
Hukumomin sun yanke hukuncin cewa jami’in ɗan sanda ASP Nuhu Usman ya aikata laifukan da suka saɓa da dokokin tsaro, da sauran sharuɗan amfani da makami.
A don haka, rundunar ƴan sanda ta kori ASP Nuhu Usman da sauran jami’an da aka kama da laifin aikata harbi ba bisa ƙa’ida ba.
Haka zalika, rundunar da za ta miƙa mutanen da suka aikata laifin zuwa ga hukumomin shari’a da ke da hurumin yanke musu hukunci.
-
News7 days ago
Wasu Kansiloli Na Zargin Ciyaman Da Daukar ‘Yan Daba Domin Kai Musu Hari A Kano
-
News5 days ago
KANO: Yara 24 Da Ake Tuhuma Da Laifi Sun Amfana Da Shirin Gyaran Tarbiya Maimakon Hukuncin Kotu A Watan Yuli
-
News7 days ago
Majalisar Dokokin Kano Ta Dakatar Da Shugabannin Kananan Hukumomin Bagwai, Rogo Da Bebeji
