News
Kotu Ta Yanke Wa Malamin Islamiyya Daurin Shekara 21 A Gidan Gyaran Hali A Kano
Wata Babbar Kotun Jihar Kano mai lamba 14, karkashin Mai Shari’a Maryam Sabo, ta yanke wa wani malamin Islamiyya, Nasif Shua’aibu ɗaurin shekara 21 a gidan gyaran hali da tarar Naira 200,00 bayan kama shi da laifin yi wa ɗalibarsa mai shekara 9 fyaɗe.
Lauyan mai gabatar da ƙara, Barista Fa’iza Dahiru Sidi, ta gabatar da shaidu guda biyar a gaban kotu, yayin da lauyan wanda ake ƙara Barista Aminu Umar ya gabatar da shaida guda ɗaya.
Amaechi Ya Caccaki Shugaba Tinubu Kan Yunwar Da Ta Addabi Ƴan Najeriya
A ƙarshe kotu ta tabbatar wa wanda ake tuhuma laifinsa, inda ta yanke hukuncin ɗaurin shekaru 14 a gidan yari kan laifin fyaɗe da kuma shekaru 7 kan laifin lalata yarinya.
Sannan kotun ta umarci wanda aka yanke wa hukuncin ya biya Naira 50,000 ga yarinyar da abin ya shafa.
