Connect with us

News

Gobara ta tashi a kasuwar Nguru ta Jihar Yobe

Published

on

FB IMG 16416356117374691
Spread the love

Daga Usman Abdullahi jibirin Nguru Yobe

Rahotanni daga jihar Yoben Najeriya na cewa gobara ta tashi a babbar kasuwar Nguru da ke jihar.

Waɗanda suka shaida lamarin sun bayyana wa indaranka cewa gobarar ta fara ne da misalin ƙarfe takwas na safiyar Asabar.

Advertisement

Sun kuma bayyana cewa gobarar ta tashi ne daga sashen ƴan takalma da kuma ƴan robobi kuma ta laƙume shaguna ba iyaka.

Tuni dai jami’an kai agaji da kuma na kashe gobara suka isa wajen domin kashe gobarar.

Mai magana da yawun ƴan sanda reshen jihar Yobe ASP Dungus Abdulkarim ya tabbatar wa indaranak da faruwar lamarin inda ya ce tuni jami’an kashe gobara da matasa suka haɗa hannu inda suke ƙoƙarin kashe gobarar.

Advertisement

Haka kuma ya tabbatar da cewa ƴan sanda da sauran jami’an tsaro sun isa wurin domin tabbatar da tsaro.

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *