News
Shekara 2 bayan hamɓare gwamnatinsa, tsohon shugaban ƙasar Mali, Boubacar Keita ya rasu
Daga Muhammad Muhammad zahraddin
Tsohon Shugaban Ƙasar Mali, Ibrahim Boubacar Keita ya rasu a yau da safe, in ji iyalin sa.
Keita ya rasu a babban birnin ƙasar, Bamako, inda ya rasu ya na da shekara 76.
Keita dai ya hau mulkin ƙasar a shekarar 2013 har zuwa 2020 lokacin da sojoji su ka hamɓare gwamnatinsa.
Wata majiya daga iyalan mamacin ta ce Keita ya rasu a yau da misalin ƙarfe 9 na safe a asibiti.
Advertisements
-
News4 days agoWasu Ƴan Daba Sun Kai Farmaki Kasuwar Siyar Da Wayoyi Ta Farm Center Dake Kano
-
News6 days agoWasu Fusatattun Matasa Sun Ƙona Mutum Uku Har lahira A Filato
-
News6 days agoAbin Takaici Ne A Kyale Mata Su Cire Wandunan Da Aka Basu Akan Titi Suna Dagawa A Cikin Al’ummar Da Ke Alfahari Da Kunya Da Addini
