News
Shekara 2 bayan hamɓare gwamnatinsa, tsohon shugaban ƙasar Mali, Boubacar Keita ya rasu
Daga Muhammad Muhammad zahraddin
Tsohon Shugaban Ƙasar Mali, Ibrahim Boubacar Keita ya rasu a yau da safe, in ji iyalin sa.
Keita ya rasu a babban birnin ƙasar, Bamako, inda ya rasu ya na da shekara 76.
Keita dai ya hau mulkin ƙasar a shekarar 2013 har zuwa 2020 lokacin da sojoji su ka hamɓare gwamnatinsa.
Wata majiya daga iyalan mamacin ta ce Keita ya rasu a yau da misalin ƙarfe 9 na safe a asibiti.
Advertisements
-
News5 days ago
Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Kai Ziyarar Ba Zata Asibitin Kwararru Na Best Choice Dake Kano
-
News6 days ago
An Tura Kwamishinonin ’Yansanda 30 Da Jami’ai 15,000 Domin Sanya Ido A Zaɓen Osun
-
News3 days ago
El-Rufa’i Ya Shigar Da Ƙarar Neman Diyyar Biliyan N10 Bisa Zargin ICPC Da Nesanta Shi Da Iyalansa
