Connect with us

News

Jiragen sojin Nijeriya sun hallaka ƴan ta’adda 20

Published

on

FB IMG 16446544768676785
Spread the love

Daga yasir sani abdullahi

 

 

Advertisement

 

Dakarun sojin sama na Nijeriya, ƙarƙashin’Operation Thunder Strike’, sun hallaka ƴan ta’adda 20 a yankin Makarantar Koyon aikin Soja.

Wasu sahihan majiyoyi na sirri sun shaidawa jaridar PRNigeria cewa an ga ƴan fashin daji a babura sama da 50 sun nufi Makarantar Koyon aikin Soja ɗin da ke Jihar Kaduna a ranar Alhamis da yamma.

Advertisement

A tuna cewa a watan Yunin 2021 ne dai ƴan bindiga su ka kutsa kai cikin makarantar, su ka kashe sojoji 2 sannan su ka yi garkuwa da Kaftin ɗin Sojan Ƙasa a yayin harin.

PRNigeria ta jiyo cewa bayan wasu bayanan sirri na yunƙurin kai harin kan makaranta, sai a ka tashi jiragen yaƙi 2 na Rundunar Sojin Sama, NAF su ka dirar wa ƴan ta’addan da a ke tsammanin sun taso ne daga ƙauyen Damari a Ƙaramar Hukumar Birnin Gwari.

An hango ƴan fashin dajin su da yawa a wasu tantuna na wucin-gadi da kuma baburan wajen 50.

Advertisement

Ganin jiragen ne ya sanya ƴan ta’addan su ka tarwatse suna neman mafaka a kuryar jeji, inda a riƙa yi musu ruwan wuta, inda a ka hango wadanda ba su mutu ba su na neman tsira.

A ranar Juma’a ne a ka samu bayanai da ga sojojin ƙasa da mazauna ƙauyuka cewa ƴan ta’addan 20 ne su ka mutu.

Advertisement

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *