Sports
Antonio Conte ya ce tawagar Tottenham ba tada karfi kamar da
Daga muhmmad muhmmad zahraddin
Kocin Tottenham, Antonio Conte ya ce tawagarsa ta rage karfi a kasuwar musayar ‘yan kwallo a watan Janairu duk da cewa sun sayi ‘yan wasa biyu.
Spurs ta dauko ‘yan wasa biyu daga Juventus Dejan Kulusevski da Rodrigo Bentancur amma sai ta bayar da aron Tanguy Ndombele da kuma Giovani lo Celso.
Sannan Dele Alli ya koma Everton a yayin da Bryan Gil ya koma taka leda a Valencia.
“Abin da ya faru a cikin watan Janairu babu sauki,” Conte ya shaidawa tashar Sky Sport Italia.
Ya kara da cewa “Mun rasa manyan ‘yan wasanmu hudu a Tottenham sai muka siyo guda biyu”.
“Ko a yawa mun ragu a maimakon karawa tawagarmu karfi.”
Conte ya koma Tottenham ne a ranar 2 ga watan Nuwambar 2021.
-
Opinion7 days ago
Ayyuka, Bin Diddigi, Biyan Kudi, Sakamako: Dabarun Kano Da Suka Zarce Jihohi 35
-
Opinion7 days ago
Tiriliyan ₦210 na Karya: Yadda Bala Wunti Ya Warware Dukkan Rudanin da Ya Mamaye Zaman Majalisar Dattawa Kan Asusun NNPC
-
News5 days ago
Likitan El-Rufai Ya Shiga Matsala Kan Zargin Bayar Da Rahoton Jinya Na Bogi
