Connect with us

News

Ku kwaikwayi taimakon al’umma a gurin A’isha Buhari, Shugaban NYSC ya shawarci attajirai

Published

on

FB IMG 1646197849350
Spread the love

Daga Muhammad Muhammad zahraddin

 

 

Advertisement

Darakta-Janar na Hukumar Bautar Ƙasa, NYSC, Shuaibu Ibrahim, ya yi kira ga attajirai da kamfanunuwan ƙasar nan da su kwaikwayi irin taimakon al’umma da Uwar gidan Shugaban Ƙasa, Aisha Buhari ta ke yi.

Ibrahim ya yi kiran ne a yayin rantsar da sabbin ƴan bautar ƙasa rukunin A, rundunar I na 2022 a sansanin horo da ke Ƙaramar Hukumar Ganjuwa, Jihar Bauchi a yau Talata.

Ya yaba wa matar shugaban ƙasar bisa Tallafin magunguna da ta baiwa hukumar NYSC, inda ya ƙara da cewa Tallafin ya taimaka wa ƴan bautar ƙasa a shirin bada magunguna kyauta a cikin ƙauyuka.

Advertisement

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *