Connect with us

News

Amurka da wasu kasashe 10 sun yi Allah wadai da harba sabon makami mai linzami da Koriya ta Arewa ta yi

Published

on

Daga kabiru basiru fulatan

 

Advertisement

 

Kasashen Amurka, Albania, Australia, Brazil, Faransa, Ireland, Japan, New Zealand, Norway, Koriya ta Kudu da Biritaniya sun fada a cikin wata sanarwar hadin gwiwa da suka fitar jiya litinin cewa Pyongyang “ta keta kudurori da dama na kwamitin sulhu.”

Advertisement

Kasashen 11 sun kuma soki Kwamitin Sulhun Majalisar Dinkin Duniya da kansa, suna mai cewa “suna ci gaba da yin shiru” yayin da Koriya ta Arewa ke kara zafafa ayyukan ta na tada zaune tsaye.

Kwamitin da ke da karfi na Majalisar Dinkin Duniya a baya-bayan nan ya kasa cimma matsaya kan matsaya guda kan ayyukan da Koriya ta Arewa ta yi a baya-bayan nan, a wani bangare na turjiya daga Rasha da China.

Advertisement

A cewar makwabciyarta, Koriya ta Kudu da Japan, a ranar Asabar din da ta gabata ne Pyongyang ta harba makami mai linzami zuwa tekun kasar, wanda shi ne gwajin makami mai linzami na Koriya ta Arewa karo na tara tun farkon wannan shekara.

Kudirin Majalisar Dinkin Duniya ya haramtawa Koriya ta Arewa, gwajin makami mai linzami, amma kasar taki.

Advertisement

Pyongyang dai na ci gaba da tayar da jijiyoyin wuya tare da harba makamai masu linzami tun farkon wannan shekara.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending