Connect with us

News

Kotu ba ta da hurumin hana mu yin gyaran fuska ga dokar zaɓe’

Published

on

Spread the love

Daga Hamza Yusuf Abdulmumin

Majalisar Dattawan Najeriya ta ce za ta ci gaba da aikinta na gyaran fuska ga sabuwar dokar zabe ta 2022 duk da umarnin da wata kotu ta bayar wanda ya dakatar da hakan.

Babbar jam`iyyar hamayyar Najeriya ce wato PDP ta kai majalisar ƙara, inda ta ƙalubalanci aikin yi wa dokar gyara bayan Shugaba Muhammadu Buhari ya rattaɓa mata hannu.

Advertisement

Amma Majalisar Dattijan ta ce kotu ba ta da hurumin hana ‘yan majalisa ayyukansu na yau da kullum.

A yayin wata tattaunawa da BBC, Sanata Kabiru Ibrahim Gaya, wanda shi ne shugaban kwamitin zaɓe na majalisar ya shaida wa BBC cewa doka ta ce babu hurumin da za a shiga da za a hana su aikin da ya kamata a yi.

Advertisement

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *