Connect with us

News

Kotu Ta Kori Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa Na Jam’iyyar AA

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja, ta umarci hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) da ta cire sunayen dukkan ‘yan takarar jam’iyyar Action Alliance (AA), ciki har da dan takarar shugaban kasa, Manjo Hamza Al-Mustapha (mai ritaya), wanda Kenneth Udeze ya mika mata.

Advertisement

 

Umurnin, wanda aka bai wa manema labarai a Kaduna a ranar Asabar din da ta gabata, ya yanke hukuncin cewa hukumar zaben ta bayyana sunayen ‘yan takarar da shugabannin jam’iyyar suka mika mata a karkashin shugabancin Adekunle Rufa’i Omoaje.

Advertisement

Chelsea da Man City na son dauko Leao, PSG na zawarcin Endrick

Kotun da ke karkashin mai shari’a Z.B Abubakar ta kuma ce hukumar zaben ta yi kuskure ne ta hanyar kasa ba da sunayen ‘yan takarar da bangaren Omoaje ya mika mata.

Advertisement

 

Omoaje a madadinsa da kungiyar Action Alliance ya tuntubi kotu domin neman hakkinsa kan rashin amincewa da ‘yan takarar da ya mika wa INEC a madadin jam’iyyar.

Advertisement

 

A hukuncin da kotun ta yanke, ana sa ran za a maye gurbin ’yan takarar da INEC ta riga ta bayyana ciki har da dan takarar shugaban kasa, Manjo Hamza Al-mustapha (mai ritaya) da jerin sunayen ‘yan takarar da Omoaje ya mika.

Advertisement

 

INEC ta bayyana Al-Mustapha a matsayin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar AA kuma tuni aka buga sunansa a shafin yanar gizon hukumar zaben.

Advertisement

 

Sai dai kuma da sabon hukuncin kotu,ana iya sanyawa a maye gurbin Al-Mustapha da wani wanda shugabancin Omoaje ya amince da shi.

Advertisement

 

Rahotannin kafafen yada labarai na cewa Al-Mustapha na iya fuskantar hadarin rasa tikitin takarar shugaban kasa na AA sakamakon karar da aka shigar akan sa.

Advertisement

 

Mai shari’a Abubakar wanda ya bayar da misali da sashe na 29 (1) na dokar zabe, 2022, ya bayar da umarnin cewa, INEC ta gaggauta fitar da sunaye da adireshi na dukkan ‘yan takarar da Omoaje ya mika a madadin kungiyar Action Alliance.

Advertisement

 

“Ta hanyar tanadin sashe na 29 (1) na dokar zabe, 2022, ya kamata INEC ta buga ta hanyar nunawa a ofishin da ya dace na INEC da kuma a shafinta na yanar gizo.”

Advertisement

 

Da yake mayar da martani game da ci gaban, Shugaban jam’iyyar AA na kasa, Adekunle Omoaje, ya ce Kenneth Udeze wanda ke nuna kansa a jam’iyyar an kore shi daga jam’iyyar tun ranar 14 ga watan Fabrairun shekarar 2020 a yayin babban taron jam’iyyar na kasa a Osogbo.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending