Connect with us

News

Amurka Da Birtaniya Sun Sassauta Matsayinsu Kan Barazanar Tsaro A Abuja

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Kasashen Amurka da Birtaniya sun tsame Babban Birnin Najeriya, Abuja, daga cikin biranen da ake fargabar yiwuwar kai harin ta’addanci a cikinsu.

Advertisement

 

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwar da Ofishin Kula da Harkokin Kasashen Waje na kungiyar Kasashen Rainon Ingila (FCDO) ya fitar.

Advertisement

Naira Ta Shiga Jerin Kudaden Da Darajarsu Ta Fi Faduwa A Duniya

Ofishin ya sanar da hakan ne a shafinsa na Intanet a daren Litinin.

Advertisement

 

Sanarwar na cewa, “Ofishin FCDO ya janye shawarar da ya ba ’yan kasashen waje a kan su guji ziyaratar Abuja in ba ya zama dole ba, sai dai har yanzu akwai burbushin hatsarin da ta yi gargadin na nan…”

Advertisement

 

Sai dai sanarwar ta ce gargadin da Ofishin ya yi na zuwa wasu garuruwa a Najeriya na nan daram.

Advertisement

 

Jihohin da ofishin ya gargadi ’yan kasashen wajen da ziyarta su ne; Borno da Yobe da Adamawa da Gombe da Kaduna da Katsina da Zamfara, da wasu jihohi na bakin teku.

Advertisement

 

Jihohin su ne; Akwa ibom, da Kuross Ribas.

Advertisement

 

Jihohin da ke da sassaucin gargadi na FCDO sun hada da Bauchi da Kano da Jigawa da Neja da Sakkwato da Kogi da kuma kilomita 20 daga bakin iyakar jihohin Neja da Kebbi.

Advertisement

 

Sai kuma jihohin Abia da Delta da Bayelsa da Ribas da Filato da kuma Taraba

Advertisement

 

Ofishin ya kuma shawarci ’yan kasashen wajen da a kodayaushe su rika bincikar sashen da ke sa ido kan shige da fice, kafin su yi duk wata tafiya don ba su shawarwari da ingantattu.

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending