News
Buhari Ya Kaddamar Da Kwalejin Sojojin Ruwa Da Sashen Tashi Da Saukar Jiragen Sama Na Kasashen Ketare A Kano
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Shugaban Kasa Muhammadu Bihari, ya kaddamar da wasu manyan ayyuka a jihar Kano dake arewa maso yammacin Najeriya.
Ayyukan sun hada da, bude kwalejin horas da sojojin ruwa, a Karamar hukumar Dawakin Tofa ( Nigerian Navy Logistics college) sai katafaren gidan gyaran hali na Janguza da kuma gyara da aka yiwa filin tashi da saukar jiragen sama na Malam Aminu Kano ( MAKIA) inda aka samar da sabon Sashen Tashi Da Saukar Jiragen Sama Na Kasashen Ketare
Jirgin Najeriya Na Shirin Keta Hazo Zuwa Birnin Abuja Daga Kasar Habasha
An kaddamar da wandan ayyuka ne ta allon-gani-ga-ka.
Shugaban ya yabawa gwamnan jihar da kuma hafsan sojin ruwa Vice Admiral AZ Gambo bisa kokarinsu na ganin an kammala aikin da kuma tabbatar da nasarar aiwatar da dukkan ayyukan.
A nasa jawabin, Ministan Tsaro, Janar Bashir Salihi Magashi, ya ce kwalejin ta yaye dalibai sau biyu, kuma za ta yaye na uku a wata na shida nan gaba, inda ya ce kwalejin na neman sahalewa daga hukumar kula da ilimin fasaha ta kasa domin a fara karatun Diploma da shaidar HND a wasu kwasa-kwasai, inda farar hula zasu fara karatu a kwalejin.
Shi kuwa gwamnan Kano, Dr Abdullahi Umar Ganduje, ya yabawa shugaban Kasar bisa wadannan muhimmanci ayyuka da shugaban Kasar ya gudanar a jihar Kano.
-
News3 days agoWasu Ƴan Daba Sun Kai Farmaki Kasuwar Siyar Da Wayoyi Ta Farm Center Dake Kano
-
News6 days agoWasu Fusatattun Matasa Sun Ƙona Mutum Uku Har lahira A Filato
-
News5 days agoAbin Takaici Ne A Kyale Mata Su Cire Wandunan Da Aka Basu Akan Titi Suna Dagawa A Cikin Al’ummar Da Ke Alfahari Da Kunya Da Addini
