Sports
Usman Abdallah Ya Ajiye Aikin Horar Da Kano Pillars
Babban kocin ƙungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars, Usman Abdallah, ya ajiye aikinsa na horas da tawagar a ranar Laraba, kamar yadda sashen yaɗa labarai na ƙungiyar ya tabbatar da hakan.
Sanarwar da aka fitar da yammacin ranar Laraba ta bayyana cewa Abdallah ya yanke shawarar barin mukaminsa ne da kansa, sai dai bai bayyana dalilan da suka sanya shi ɗaukar wannan mataki ba.
A halin da ake ciki, magoya bayan Pillars na ci gaba da bayyana ra’ayoyinsu a kafafen sada zumunta dangane da ficewar Abdallah, inda da dama ke bayyana fatan ganin sabon babi mai armashi a tarihin ƙungiyar.
-
News4 days ago
Hukumar Kula Da Harkokin Shari’a Ta Tilasta Wa Alƙali Ritaya Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Naira 250,000 A Kano
-
News5 days ago
Jigawa: Sama da Gine-gine 200 Sun Lalace Sakamakon Iska Da Ruwan Sama Mai Ƙarfi
-
News4 days ago
Wasu Fusatattun Matasa Sun Hallaka Wani Mutum Tare Da Kona Gawarsa Kan Zargin Satar Babur A Kano
