Sports
Usman Abdallah Ya Ajiye Aikin Horar Da Kano Pillars
Babban kocin ƙungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars, Usman Abdallah, ya ajiye aikinsa na horas da tawagar a ranar Laraba, kamar yadda sashen yaɗa labarai na ƙungiyar ya tabbatar da hakan.
Sanarwar da aka fitar da yammacin ranar Laraba ta bayyana cewa Abdallah ya yanke shawarar barin mukaminsa ne da kansa, sai dai bai bayyana dalilan da suka sanya shi ɗaukar wannan mataki ba.
A halin da ake ciki, magoya bayan Pillars na ci gaba da bayyana ra’ayoyinsu a kafafen sada zumunta dangane da ficewar Abdallah, inda da dama ke bayyana fatan ganin sabon babi mai armashi a tarihin ƙungiyar.
-
News7 days ago
Wasu Kansiloli Na Zargin Ciyaman Da Daukar ‘Yan Daba Domin Kai Musu Hari A Kano
-
News5 days ago
KANO: Yara 24 Da Ake Tuhuma Da Laifi Sun Amfana Da Shirin Gyaran Tarbiya Maimakon Hukuncin Kotu A Watan Yuli
-
News4 days ago
ICPC Ta Wanke Femi Gbajabiamila Daga Zargin Badakalar Hukumar Bogi
