Connect with us

News

Me Ake Ciki?: Bayan APC Ta Dage Kaddamar Da Kwamitin Yakin Neman Zabe

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Har yanzu dai jam’iyyar APC mai mulki ba ta fara yakin neman zaben shugaban kasa na 2023 ba, kwanaki bakwai bayan da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta dage haramcin yakin neman zabe.

 

Advertisement

 

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta dage haramcin fara yakin neman zabe a hukumance a ranar 28 ga watan Satumba, sai dai Daily Trust ta ruwaito cewa har yanzu jam’iyyar APC ta kasa shawo kan rikicin da ke tsakaninta da kwamitin yakin neman zaben.

Advertisement

Gwamnatin Kwara Ta Dakatar Da Likitan Da Ake Zargi Da Hallaka Wasu Mata A Jihar

Kafin kaddamar da yakin neman zaben, sakataren kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar APC, James Faleke, ya fitar da jerin sunayen mutane 422 na kwamitin.

Advertisement

 

Sai dai ci gaban ya samu tirjiya da kalubale daga masu ruwa da tsaki na jam’iyyar da suka hada da kwamitin ayyuka na kasa (NWC) da gwamnonin da ‘ya’yan jam’iyyar kamar yadda suka yi ikrarin ba a tafi da su a cikin shirin.

Advertisement

 

Biyo bayan cece-kuce da rashin jituwar da akan jerin sunayen, babban daraktan kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar APC kuma gwamnan jihar Filato, Simon Lalong, ya sanar da dage bikin rantsar da su.

Advertisement

 

Sai dai wata majiya daga jam’iyyar ta APC ta shaida wa wakilinmu a jiya cewa gwamnoni da NWC da sauran masu ruwa da tsaki na jam’iyyar na ci gaba da gudanar da ayyuka daban-daban, wanda hakan ya sa aka samu tsaikon yin sabon jerin sunayen da kaddamar da kwamitin.

Advertisement

 

Sai dai kakakin kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar APC da babban daraktan yada labarai, Festus Kayamo da Bayo Onanuga, ba su amsa kira ba, ko kuma amsa sakon SMS da aka aika a wayoyinsu domin jin ta bakinsu kan lamarin.

Advertisement

 

 

Advertisement

Lalong da sauran gwamnonin APC sun gana kan yakin neman zaben 2023

 

Advertisement

Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa, Babban daraktan yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar APC kuma gwamnan jihar Filato, Simon Lalong a ranar Talata ya gana da wasu gwamnonin ‘yan kwamitin yakin neman zaben jam’iyyar don tsara dabarun zaben 2023.

 

Advertisement

Taron ya gudana ne a shedikwatar kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar APC da ke tsakiyar yankin kasuwanci a Abuja.

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Majalisar Dattawa a ranar Talata ta bukaci Kamfanin Gas na Najeriya (NLNG) Limited da ya biya diyyar Naira biliyan 18.4 ga kusan iyalai 200 da aka saye gonakinsu a Bonny na Jihar Ribas kan hakkin mallakar bututun mai.

 

Advertisement

Jaridar indaranka ta rawaito cewa, Hakan ya biyo bayan nazari da amincewa da rahoton kwamitin da’a, gata da kararrakin jama’a wanda ya binciki karar da al’ummomin suka

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending