Connect with us

Entertainment

Mai Kwashewa Ya Samu Digirin Girmamawa A Togo

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Wata jami’a a kasar Togo ta karrama fitaccen mai shirya fina-finai na masana’antar Kannywood, Abdulrahman Muhammad wanda aka fi sani da Abdul Amat Mai Kwashewa da digirin girmamawa.

 

Advertisement

Jami’ar mai suna IHIRIS ta ba Furodusan digirin-digirgir na Dokta a fannin Sha’anin Mulki da kuma Gudanarwa.

 

Advertisement

An Sace Mataimakin Daraktan IAR Da Ke Zariya

An ba matashin digirin ne a wani kwarya-kwaryar biki a harabar jami’ar da ke Togo a cikin jerin bukukuwan yaye dalibanta a karshen makon nan.

 

Advertisement

A hirar da Aminiya ta yi da Nura Shariff, daya daga cikin na hannun daman Abdul din, ya ce jami’ar ta ba shi digirin girmamawar ne sakamakon wani zuzzurfan bincike da kuma bibiyar ayyukansa na taimakon matasa.

 

Advertisement

Sannan bayan dogon nazari, sai ta ga ya cancanta ta karrama shi da digirin domin ya zama abin misali da kuma koyi ga ’yan baya.

 

Advertisement

Matashin dan siyasan ya yi fice a wajen taimakon jama’a musamman ’yan Kannywood da jikinsa da kuma aljihunsa.

 

Advertisement

Shi ya kafa kungiyar YBN don tallata takarar Gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello ta shugaban kasa, a yanzu kuma shi ne Babban Darktan yakin neman zaben Tinubu a bangaren fadakarwa da nishadantarwa.

 

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending