Entertainment
Qatar 2020: FIFA ta kuma zabo mawakin Najeriya Kizz Daniel
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Tauraron mawakin Najeriya, Kizz Daniel, ya shiga cikin jerin fitattun mawaka da za su taka rawa a gasar cin kofin duniya na 2022 a Qatar.
Kizz Daniel shi ne dan Najeriya na biyu maiwaki da FIFA ta zabo domin faranta ran magoya bayan gasar kwallon kafa ta duniya.
INEC ta fara kafe rajistar sunayen masu kaɗa ƙuri’a a faɗin Najeriya
Hukumar kula da kwallon kafa ta duniya a makon da ya gabata ta sanya Patoranking cikin fitattun taurarin mawakan da za su hau matakin a babban filin wasa na Qatar a ranar farkon bude wasan.
Mawakan biyu za su yi waka a Doha a ranar 23 ga Nuwamba.
Sunan Kizz Daniel na ainihi shine Oluwatobiloba Daniel Anidugbe.
Shi ne wanda ya lashe lambar yabo da yawa na Nigerian Afrobeats, Pop, R&B mawaƙin, kuma marubucin waƙa tare da fitattun waƙoƙi irin su Woju, Buja, Cough da sauran su.
