Connect with us

Entertainment

Matan Kannywood Sun Ziyarci Shugaban Hisbah A Kano

Published

on

Babban Kwamandan Hukumar Hisbah na Jihar Kano, Sheik Harun Ibn Sina

 

Matan Kannywood Sun Ziyarci Shugaban Hisbah A Kano

Advertisement

Babban Kwamandan Hukumar Hisbah na Jihar Kano, Sheik Harun Ibn Sina

 

Advertisement

 

Kungiyar Jarumai Mata A Masana’atar Kannywood (AKAFA) ta ziyarci Shugaban Hukumar Hisbah ta Jihar Kano, Uztaz Haroun Muhammad Ibn Sina, a ofishinsa.

Advertisement

 

Hukumar ta bayyana ta shafinta na Facebook cewa kungiyar ta kai ziyarar ce a karkashin shugabarta, Rashida Abdullahi Mai Sa’a.

Advertisement

 

 

Advertisement

Shugaban Hukumar kuma Babban Kwamandan Hisbah a Kano, ya bayyana farin ciki da ziyarar, duba da cewa manufofin kungiyar sun yi daidai da ayyukan hukumarsa na dakile ayyukan barna.

 

Advertisement

Hukumar ta kuma amince ta bai wa kungiyar matan na Kannywood goyon baya wajen cim-ma manufofinta na gyara a sana’arsu ta fina-finan Hausa.

 

Advertisement

A nata jawabin, Mataimakiyar Babban Kwamandar Hisbah, Ummu Kulthum Kassim, ta yaba wa kungiyar bisa shirinta na tsaftace harkar fina-finan Kannywood, da kuma yadda wasu daga cikin jaruman Kannywood mata ke kokarin kyautata mu’amalarsu da kuma kamun kai.

 

Advertisement

A jawabinsa, Mashawarcin Gwamnan Kano kan Hukumar Hisbah, Mujjitaba Baban Usama, kira ya yi ga matan da su tsarkake niyyarsu da kuma aiki don Allah.

 

Advertisement

Tun da farko, a jawabin shugabar kungiyar, Rashida Abdullahi Mai Sa’a a, ta ce sun kawo ziyara ne don gabatar da sabuwar kungiyarsu ta AKAFA da manufofinta ga hukumar, da nufin tsaftace harkar fim.

 

Advertisement

A baya dai Hukumar Hisbah ta sha kamen mata a matattarar yin badala da gantali, wadanda ta ce ’yan fim ne.

 

Advertisement

 

DAILY TRUST

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending