Connect with us

News

Hukumar Hisbah Ta Kama Matasa Maza Da Mata Su 20 Saboda Suna Wanka Tare A Kano 

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

Hukumar ta Hisbah dake yaki da rashin da’a ta yi kamen ne a wani wurin shakatawa biyo bayan korafe-korafen da wasu mazauna yankin suka yi, a cewar kafafen yada labaran Najeriya.

Mataimakin kwamandan hukumar Dr. Mujahidin Aminuddin Abubakar ya tabbatar da faruwar lamarin.

Advertisement

Yadda Ƴan ta’adda suka dagargaza ƙauyuka 50, suka sace daruruwan mutane a Zamfara 

Da yake karin haske kan yiwuwar sun aikata laifi, Dr. Abubakar ya ce wannan aika-aikar ta saba wa dokar Hisbah, wacce ta haramta wa maza da mata wanka tare.

Dr. Abubakar ya kara da cewa, da zarar aka kammala bincike za a hukunta wadanda ake zargi da aikata laifin. Ya kuma yi kira ga iyaye da su sa ido sosai kan harkar ‘ya’yansu.

Advertisement

Idan ba a manta ba, a baya-bayan nan, Hukumar ta gayyaci Murja Ibrahim Kunya, wadda ta yi suna a kafar Tik Tok, tare da wasu zuwa hedikwatar hukumar saboda ta yiwu suna bukatar gyaran hali.

Hakan dai na zuwa ne bayan da hukumar ta tsare Murja tare da wasu, saboda yin abubuwan da hukumar ta ce basu dace ba a shafukan sada zumunta a shekarar 2023.

Advertisement

A yanzu dai hukumar na bi a hankali wajen kawar da rashin da’a musamman a kafafen sada zumunta.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending