Connect with us

News

Yan Sanda Sun Kama Maharan Da Suka Addabi Abuja Da Nasarawa

Published

on

DAGA MARYAM BASHIR MUSA 

 

Advertisement

 

Rundunar ’Yan Sandan babban birnin tarayya, ta cafke gungun wasu mutum 10 da ake zargin su da kai hare-hare a Abuja da Jihar Nasarawa.

Advertisement

 

Da yake gabatar da su a gaban manema labarai, Kwamishinan ’Yan Sandan Babban Birnin Tarayya, Sadiq Abubakar, ya ce an kama wadanda ake zargin a wani otel da ke yankin Masaka, kilomita kadan zuwa Abuja.

Advertisement

 

Karin Albashi: Gwamnati Ta Lashe Amanta

An samu bindiga kirar AK-47 guda biyar, sai kwanson harsashi 22 da kuma kananan bindigogi guda uku.

Advertisement

 

Ragowar abubuwan da aka samu a wajensu sun hada mota kirar Toyota Camry 2000, katin aikin wani dan sanda da kuma janareto guda biyu.

Advertisement

 

 

Advertisement

Kazalika, rundunar ta cafke wasu bata-gari hudu da ake zargi da aikata fashi da makami a unguwar Maitama da ke Abuja.

 

Advertisement

Har wa yau, wadanda ake zargin sun yi wa wani mai sana’ar POS fashin kudi.

 

Advertisement

An samu karamar bindiga guda uku da harsashi 14, talabijin guda biyu, wayoyin hannu da kuma kayan yari da ake zargin fashin su suka yi.

 

Advertisement

Rundunar ta kuma gano maboyar wasu masu kai wa ’yan bindiga makamai ne.

 

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending