News
Karin Albashi: Gwamnati Ta Lashe Amanta
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Gwamnatin Tarayya ta lashe amanta kan batun karin albashin ma’aikata a shekarar 2023 mai kamawa.
Gwamnatin ta bayyana cewa ba ta da niyyar kara wa ma’aikatanta albashi kamar yadda wasu kafafen yada labarai ke rade-radi.
Ta bayyana cewa sabanin karin albashi da ake rade-radi, “wasu alawus-alawus kawai” take shirin kara wa ma’aikata.
Ministan Kwadago, Chris Ngige, ne ya sanar da haka ta wata sanarwa da mai magana da yawun ma’aikatarsa, Olajide Oshundun ya fitar a ranar Juma’a.
Advertisements
