News
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Alhamis A Matsayin Ranar Hutu
Gwamnatin Tarayya ta bayyana Alhamis, 12 ga Yuni, a matsayin ranar hutu domin bikin Ranar Dimokuraɗiyya ta shekarar 2025.
Sanarwar ta fito ne daga Ministan Harkokin Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo, ta bakin Babbar Sakatariyar Ma’aikatar, Magdalene Ajani, a ranar Lahadi.
Gwamnatin Kano Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Biya Diyya Kan Soke Hawan Sallah
Ministan ya taya ’yan Najeriya murnar cika shekaru 26 da komawar ƙasar mulkin farar hula, yana mai yabawa da juriya da ƙwazo da al’umma ke nunawa wajen ganin dimokuraɗiyya ta dore.
Ya ce, “a ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, Najeriya na ci gaba da mutunta ƙa’idodin dimokuraɗiyya, kuma ra’ayoyin jama’a na taka muhimmiyar rawa wajen tsara harkokin siyasa, tattalin arziki da rayuwar yau da kullum.”
Gwamnatin ta kuma bukaci ’yan ƙasa da su ci gaba da bayar da gudunmawarsu wajen tabbatar da zaman lafiya da cigaban ƙasa.
