Connect with us

News

Gwamnatin Kano Ta Rufe Film House Da Ke Unguwar Dorayi. ‎

Published

on

IMG 20260624 WA0031 768x765

‎Gwamnatin Jihar Kano ta kulle wata cibiyar harkokin fina-finai da ke Unguwa Bello a yankin Dorayi, bisa zargin karya dokokin tsara gine-gine da kuma gudanar da aiki a yankin da aka ware domin gidajen zama.

‎An aiwatar da matakin ne a ranar Laraba a ƙarƙashin shirin “Operation Show Your Document”, wanda Kwamitin Yaƙi da Gine-ginen da Ba Su da Izini ke gudanarwa ƙarƙashin jagorancin Babban Daraktan Hukumar Kula da Taswirar Filaye da Kasa (KANGIS) na jihar Kano, Dakta Dalhatu Sani Aliyu

Advertisement

KANO: Kwamitin Binciken KNUPDA Ya Buɗe Karɓar Ƙorafe-Ƙorafe Da Shawarwarin Jama’a

‎Da yake jawabi yayin aikin, Dakta Dalhatu ya ce matakin ya biyo bayan korafe-korafen da mazauna yankin da wasu malamai suka shigar kan yadda ake gudanar da cibiyar a cikin unguwar.

Advertisement

‎Ya bayyana cewa binciken farko da kwamitin ya gudanar ya nuna cewa cibiyar ba ta cika wasu muhimman sharuddan doka da suka wajaba ba.

‎“Mun samu korafe-korafe daga al’umma da kuma wasu malamai kan wannan cibiya. Bayan binciken da muka fara gudanarwa, mun gano akwai matsaloli da dama, kuma har yanzu ba a gabatar mana da takardun da suka dace ba,” in ji shi.

Advertisement

‎Shugaban KANGIS ya kara da cewa ko da masu cibiyar suka gabatar da wasu takardu a gaba, har yanzu za a ci gaba da kallon ginin a matsayin wanda ya saɓa wa dokokin tsara birane saboda wurin da aka kafa shi.

‎“Ana magana ne kan yanki da kusan kashi 99 cikin 100 na gidajen zama ne. Saboda haka kafa cibiyar harkokin fina-finai a irin wannan muhalli ya saɓa wa dokokin amfani da ƙasa da tsarin gine-gine,” ya bayyana.

Advertisement

‎Dakta Dalhatu ya ce gwamnatin jihar na kuma la’akari da tasirin irin waɗannan ayyuka ga zamantakewar al’umma, musamman matasa, domin tabbatar da kyawawan ɗabi’u da ingantacciyar tarbiyya a tsakanin al’umma.

‎Ya yi gargaɗin cewa gwamnati ba za ta yi sassauci ga duk wani mutum ko ƙungiya da ke gudanar da ayyuka ba tare da bin tanade-tanaden doka ba.

Advertisement

‎“Duk wanda yake tunanin ya fi ƙarfin doka, to doka za ta yi aiki a kansa cikin adalci da sahihiyar hanya,” in ji shi.

‎Sannan ya tabbatar wa mazauna yankin cewa gwamnatin jihar za ta ci gaba da sauraron korafe-korafensu tare da ɗaukar matakan da suka dace domin kare muradunsu.

Advertisement

‎A cewarsa, wannan mataki na daga cikin ci gaba da ƙoƙarin gwamnatin jihar na tabbatar da bin dokokin tsara birane tare da magance gine-gine da ayyukan da ake gudanarwa ba bisa ƙa’ida ba a sassa daban-daban na Kano.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending