News
Rundunar Sojin Najeriya Ta Ayyana Neman Jami’inta Ruwa A Jallo Kan Zargin Taimaka Wa ‘Yan Ta’adda
Rundunar Sojin Najeriya ta ayyana wani jami’inta, Private Mohammed Yusuf Amutu, a matsayin wanda ake nema ruwa a jallo bisa zargin sayar wa ‘yan ta’adda da sauran masu aikata laifuka kayan aikin soja.
A cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar, ta ce binciken farko ya nuna cewa jami’in, wanda ke aiki a Nigerian Army Ordnance Kits Factory, ya tsere daga sansaninsa tun ranar 3 ga Yunin 2026, kuma tun daga lokacin ba a san inda yake ba.
Aƙalla Fasinjoji 68 Ne Suka Tsallake Rijiya Da Baya A Jirgin Enugu Air
Sanarwar ta bayyana cewa ana neman jami’in ne domin ya amsa tambayoyi kan zargin da ake masa na sayar da kayan aikin soja ga masu aikata laifuka.
Rundunar ta ce ba za ta yi sassauci da duk wani jami’in da zai yi amfani da aikinsa wajen taimaka wa ‘yan ta’adda ko wasu masu aikata laifuka ba. Ta jaddada cewa duk wanda aka samu da hannu a irin wannan laifi zai fuskanci hukunci mai tsanani bisa dokokin soja da na kasa.
Har ila yau, rundunar ta yi kira ga al’umma da su bai wa jami’an tsaro sahihan bayanan da za su taimaka wajen gano inda jami’in yake domin ci gaba da bincike.
Ta kuma tabbatar da cewa za ta ci gaba da daukar matakan da suka dace wajen kare tsaron kasa da kuma tabbatar da mutuncin Rundunar Sojin Najeriya.
-
Opinion5 days ago
Ayyuka, Bin Diddigi, Biyan Kudi, Sakamako: Dabarun Kano Da Suka Zarce Jihohi 35
-
Opinion4 days ago
Tiriliyan ₦210 na Karya: Yadda Bala Wunti Ya Warware Dukkan Rudanin da Ya Mamaye Zaman Majalisar Dattawa Kan Asusun NNPC
-
News3 days ago
Likitan El-Rufai Ya Shiga Matsala Kan Zargin Bayar Da Rahoton Jinya Na Bogi
