Connect with us

News

An haramta wa gwamnatoci cire tsabar kuɗi daga asusu a Najeriya

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN

Hukumar da ke yaƙi da laifukan da suka shafi hada-hadar kuɗi a Najeriya, NFIU, ta ce dokar hana cire tsabar kuɗi daga asussan gwamnati a kowane mataki za ta fara aiki daga ranar ɗaya ga watan Maris mai zuwa.

Advertisement

An Rufe Gidajen Mai 14 A Kano Saboda Sayarwa A Farashin Da Ya Wuce Hankali

A cewar hukumar Nigeria Financial Intelligence Unit (NFIU), duk wani jami`in gwamnati da ya taka dokar zai fuskanci ɗaurin shekara uku a gidan yari ko kuma tarar da za ta kai ninkin kuɗin da ya cira sau uku.

Advertisement

Shugaban NFIU Malam Modibbo Hamman Tukur ya faɗa wa BBC Hausa cewa tun daga lokacin da gwamnatin Buhari ta fara mulki an cire jimillar garin kuɗi naira biliyan 225 daga asusun gwamnatin tarayya.

“Gwamnatocin jiha ne suka fi cirar kuɗin, inda aka ɗauki garin kuɗi biliyan 700. Gwamnatocin ƙananan hukumomi kuma biliyan 156 kawai suka cira,” in ji shi.

Advertisement

Danna hoton ƙasa ku saurari cikakkiyar hirar da Ibrahim Isa ya yi da Malam Modibbo:

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending