Connect with us

News

Buhari Ya Kaddamar Da Kwalejin Sojojin Ruwa Da Sashen Tashi Da Saukar Jiragen Sama Na Kasashen Ketare A Kano

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN

 

Advertisement

Shugaban Kasa Muhammadu Bihari, ya kaddamar da wasu manyan ayyuka a jihar Kano dake arewa maso yammacin Najeriya.

Ayyukan sun hada da, bude kwalejin horas da  sojojin ruwa, a Karamar hukumar Dawakin Tofa ( Nigerian Navy Logistics college) sai katafaren gidan gyaran hali na Janguza da kuma gyara da aka yiwa filin tashi da saukar jiragen sama na Malam Aminu Kano ( MAKIA) inda aka samar da sabon  Sashen Tashi Da Saukar Jiragen  Sama Na Kasashen Ketare

Advertisement

Jirgin Najeriya Na Shirin Keta Hazo Zuwa Birnin Abuja Daga Kasar Habasha

An kaddamar da wandan ayyuka ne ta allon-gani-ga-ka.

Shugaban ya yabawa gwamnan jihar da kuma hafsan sojin ruwa Vice Admiral AZ Gambo bisa kokarinsu na ganin an kammala aikin da kuma tabbatar da nasarar aiwatar da dukkan ayyukan.

Advertisement

A nasa jawabin, Ministan Tsaro, Janar Bashir Salihi Magashi, ya ce  kwalejin ta yaye dalibai  sau biyu, kuma za ta yaye na uku a wata na shida nan gaba, inda ya ce kwalejin na neman sahalewa daga hukumar kula da ilimin fasaha ta kasa domin a fara karatun  Diploma da shaidar HND a wasu kwasa-kwasai, inda farar hula zasu fara karatu a kwalejin.

Shi kuwa gwamnan Kano, Dr Abdullahi Umar Ganduje, ya yabawa shugaban Kasar bisa wadannan muhimmanci ayyuka da shugaban Kasar ya gudanar a  jihar Kano.

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending