Connect with us

News

Kotu Ta Sake Haramta Wa Ƴan Sanda Tilasta Bin Dokar Amfani Da Gilashi Mai Duhu

Published

on

tinted glasses.png 1

Babbar Kotun da ke zaune a Jihar Delta ta fitar da umarnin hana Sufeto Janar na ƴan sanda (IGP) da Hukumar ƴan sanda komawa tilasta wa masu ababen hawa bin dokar amfani da gilashi mai duhu a faɗin Nijeriya.

Mai Shari’a Joe Egwu a ranar Laraba yayin gabatar da umarnin, ya kuma haramta wa ƴan sanda cin mutunci, kamawa ko tatsar masu ababen hawa kuɗaɗe akan al’amarin.

Advertisement

Zargin Bai Wa ’Yan Bindiga Makamai: DSP Ya Harbe Kansa A Jihar Neja

Kotun ta ce, umarnin zai cigaba da aiki ne daga yanzu har sai zuwa lokacin da za a gudanar da shari’ar da aka shigar akan batun.

Hakan na zuwa ne bayan da wani mai suna Mista Israel Joe ta lauyansa Kunle Edun ya shigar da ƙara a jihar bisa matakin da hukumar ta ɗauka na aiwatar da dokar.

Advertisement

A ranar Litinin ne kakakin rundunar ƴan sanda, Benjamin Hundeyin ya sanar komawa amfani da dokar, wadda da za ta fara aiki a ranar 2 ga watan Junairun 2026.

Tuni kotun ta ayyana ranar 24 ga watan Disambar 2025 domin sake sauraron ƙarar al’amarin.

Advertisement

 

 

Advertisement

BLUEPRINT

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending