News
Za A Gurfanar Da Sojoji 36 Da Ake Zargi Da Yunkurin Kifar Da Gwamnatin Shugaba Tinubu
A wannan Jumma’a ake gurfanar da sojoji 36 da ake zargi da yunkurin juyin mulki ga Shugaban Najeriya Bola Tinubu, gaban Kotun Soji na musamman a Abuja, bayan da Hedikwatar Tsaro ta kafa kwamitin masu shari’a.
Hedikwatar Tsaro ba ta yi wani sanarwa kan matakin ba, sai dai rahotanni na cewa kotun za ta yi zamanta a ɗakin taron manyan hafsohi na Scorpion da ke Asokoro a babban birnin tarayya Abuja a ranar 23 ga wataan Afrilu, bisa ga umarnin da AM Alechenu, Kwamandan sashin Garrison na Hedikwatar Tsaro ya sanya wa hannu.
Umarnin, wanda aka sanya wa hannu a ranar 17 ga watan Afrilu, ya bayyana cewa haɗakar ‘yan sandan soji da ‘yan sandan ruwa da na sama, gami da jami’an tsaron fadar shugaban ƙasa za su yi gadin kotun.
Umurnin ya ce, ba amince kowa ya shigo da makamai cikin ɗakin shari’ar ba, sai masu gadin kotu waɗanda aka ba su izinin.
A cewar umarnin, an kafa tawagar masu shari’ar ne bisa ga Dokar Sojojin ta Cap A20 ta Dokokin Tarayyar Najeriya ta shekarar 2004.
Tawagar alkalan ta ƙunshi manyan hafsoshi daga Sojojin Ruwa da Sama da kuma na ƙasa ƙarƙashin wani babban jami’i.
Waɗanda za a gurfanar na daga cikin wani rukunin jami’an tsaro da aka tsare tun shekarar 2025, sakamakon zarginsu da yunkurin juyin mulki da bai yi nasara ba.
Lamarin ya fara fita ne tamkar jita-jita, cewa an kama wasu jami’ai kan zargin juyin mulki, sai dai hukumomi harda rundunar sojin Najeriya sun yi watsi da ikirarin, kafin daga bisani suka amince cewa shirin kifar da gwamnatin Mista Tinubu gaskiya ne.
Yunkurin juyin mulki da ake zargi ya shafi fararen hula da tsoffin sojoji da kuma jami’ai dake aiki.
An gurfanar da wasu fararen hula da tsoffin sojoji biyu gaban babbar kotun tarayya dake Abuja bayan da gwamnatin Najeriya ta shigar da tuhume-tuhume 13 a kansu.
Tuhume-tuhumen wanda Rotimi Oyedepo, jagoran Lauyoyin gwamnatin Tarayya, wanda ke aiki a madadin Ofishin Babban Lauyan Tarayya ya sanya hannu a kansu, sun haɗa da cin amanar ƙasa, ta’addanci, rashin fallasa laifi da kuma halatta kudaden haram.
Cikin waɗanda ake tuhumar harɗa Mohammed Ibrahim Gana, manjo janar mai ritaya; Erasmus Ochegobia Victor, kyaftin din sojojin ruwa mai ritaya; Ahmed Ibrahim, sufeto na ‘yan sanda; da Zekeri Umoru, wani mai gyaran wutar lantarki a Fadar Shugaban Kasa. Sauran sun haɗa da Bukar Kashim Goni da Abdulkadir Sani, wani malamin addinin Musulunci da ke Zariya, wanda tsare shi ya fi ɗaukar hankali tare da haifar da cece-kuce.
Ga sunayen sojoji dake aiki 36 da za’a gurfanar kan yunkurin juyin mulki.
1
MA Sadiq
Brigadier General
N/10321
2
MA Ma’aji
Colonel
N/10668
3
IM Hussain
Lieutenant Colonel
N/12225
4
M Almakura
Lieutenant Colonel
N/12983
5
P Dangnap
Lieutenant Colonel
N/13025
6
S Bappah
Lieutenant Colonel
N/13036
7
AA Hayatu
Lieutenant Colonel
N/13038
8
SM Gana
Lieutenant Colonel
N/13857
9
IU Yusuf
Wing Commander
NAF/3117
10
MM Jiddah
Major
N/13003
11
H Yusuf
Major
N/13877
12
AD Dauda
Major
N/14394
13
JM Ganaks
Major
N/14363
14
D Yusuf
Major
N/14753
15
J Iliyasu
Major
N/14837
16
MA Usman
Major
N/15404
17
A Mohammed
Major
N/15769
18
II Idris
Major
N/16185
19
DB Abdullahi
Lieutenant Commander
NN/3289
20
SB Adamu
Squadron Leader
NAF/3481
21
NG Zuzu
Squadron Leader
NAF/3617
22
G Binuga
Captain
N/16722
23
I Bello
Captain
N/16266
24
AA Yusuf
Captain
N/16724
25
IU Zubair
Captain
N/17646
26
ML Muhammad
Captain
N/18445
27
SS Felix
Lieutenant
N/18105
28
Nasiru Ibrahim
Warrant Officer
95NA/39/2281
29
Abdul Abdullahi
Staff Sergeant
99NA/48/126
30
Alhassan Zakari
Sergeant
97NA/44/4394
31
Sanda Usman
Sergeant
03NA/54/5529
32
Abubakar Ibrahim
Sergeant
06NA/58/3829
33
Momoh Audu
Corporal
96NA/41/1592
34
Aliyu Ibrahim
Corporal
10NA/65/7797
35
Sambo Danladi
Lance Corporal
16NA/75/634
