News
Za’a Yi Kidayar ‘yan Kasa a Watan Mayu
Daga Yasir sani Abdullah
Za a yin kidayar ‘yan kasa a watan Mayu mai zuwa, bayan shekara 15 da aka taba yin kidayar, a cewar shugaban hukumar kidaya ta Nijeriya National Population Commission.
Shugaban Hukumar, Nasir Isa Kwarra ya ce fasahar zamani za ta taimaka wajen tabbatar da cewa an gudanar da sahihiyar kidaya da ake sa ran za a gudanar a watan Mayu mai zuwa.
Wasu ‘yan kungiyoyin kudancin Nijeriya ba su yarda da sakamakon kidayar da aka yi ba a shekarar 2006, suna masu zargin magudi don fifita yankin arewacin Nijeriya.
Kiyasi ya nuna cewa al’ummar Nijeriya sun kai miliyan 200, idan aka kwatanta da miliyan 140 da aka samu a shekarar 2006.
-
News4 days agoWasu Ƴan Daba Sun Kai Farmaki Kasuwar Siyar Da Wayoyi Ta Farm Center Dake Kano
-
News6 days agoWasu Fusatattun Matasa Sun Ƙona Mutum Uku Har lahira A Filato
-
News6 days agoAbin Takaici Ne A Kyale Mata Su Cire Wandunan Da Aka Basu Akan Titi Suna Dagawa A Cikin Al’ummar Da Ke Alfahari Da Kunya Da Addini
