News
Kofin duniya ya matso, Ku karawa Super Eagles kwarin gwiwa – Buhari ga ‘yan Najeriya
Advertisements

Daga kabiru basiru fulatan
Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya mayar da martani kan rashin nasarar da kungiyar kwallon kafa ta Super Eagles ta Najeriya ta yi a kasar Tunisia a ranar Lahadi, 23 ga watan Janairu a birnin Garoua na kasar Kamaru.
Shugaban ya ce duk da cewa kungiyar ba ta kai yadda ‘yan Najeriya ke zato ba a gasar #AFCON ba, jami’ai da ‘yan wasa sun cancanci a yaba musu kan gwagwarmayar da suka yi.
Shugaba Buhari ya bukaci ‘yan Najeriya da su kara wa ‘yan wasan kwarin gwiwar yin abin da ya dace a karo na gaba, musamman ganin yadda wasannin neman gurbin shiga gasar cin kofin duniya da aka shirya musu.
Advertisements
