News
Buhari ya soke zuwa Zamfara
Daga kabiru basiru fulatan
Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya soke ziyarar da zai kai Jihar Zamfara a yau Alhamis.
Gwamnan Jihar Zamfara, Bello Matawalle me ya baiyana hakan.
A jiya Laraba ne dai Gwamnan ya baiyana cewa Buhari zai kai ziyarar a yayin wani taron gaggawa da ya yi da ɗaukacin masu rike da muƙaman siyasa a zauren majalisar zartsawar jihar a ranar Talata da daddare.
A cewar Matawalle, makasudin ziyarar shugaban kasar shine jajantawa kan hare-haren ta’addancin da a ka kai ƙananan hukumomin Anka da Bukkuyum, inda aka kashe mutane da dama.
Amma kuma a wata sanarwa da ta fita a yau, Matawalle ya ce Buhari ya soke ziyarar ne sakamakon rashin kyawun yanayi.
Sai dai kuma ya ce shugaban ƙasar zai sake sanya wani lokacin domin ya kai ziyarar ta jaje da ta’aziyya a jihar a makon gobe.
-
News3 days agoWasu Ƴan Daba Sun Kai Farmaki Kasuwar Siyar Da Wayoyi Ta Farm Center Dake Kano
-
News5 days agoWasu Fusatattun Matasa Sun Ƙona Mutum Uku Har lahira A Filato
-
News5 days agoAbin Takaici Ne A Kyale Mata Su Cire Wandunan Da Aka Basu Akan Titi Suna Dagawa A Cikin Al’ummar Da Ke Alfahari Da Kunya Da Addini
