Connect with us

News

Ciwon kunne ya sa an ɗage shari’ar ‘Ɗan Sarauniya’ Jin sa ya dauke

Published

on

FB IMG 16434118875820638
Spread the love

Daga Usman abdullahi jibrin

 

 

Advertisement

Wata kotu a Kano ta ɗage zaman farko da aka soma a yau bayan an gurfanar da tsohon Kwamishinan Ayyuka na jihar, Mu’azu Magaji.

Lauyan wanda ake zargin ya bayyana cewa an ɗage shari’ar ne sakamakon matsala da kunnen wanda ake zargin yake da shi biyo bayan hatsarin motar da ya yi a Abuja bayan yan sanda sun biyo shi.

Lauyansa, Barrista Garzali Datti Ahmad ya shaida wa BBC cewa sun gaya wa kotu cewa ba za a iya karanta wa wanda ake zargin laifinsa ba sakamakon ba ya ji sosai, ganin cewa a lokacin da ya yi hatsarin, balan-balan ta kariya wadda aka fi sani da “Airbag” ta fito ta daki kunnensa.

Advertisement

Ya bayyana cewa a halin yanzu kotu ta bayar da umarni a mayar da shi asibitin ƴan sanda da ke Bompai a Kano domin a ci gaba da duba lafiyarsa.

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *