News
Ciwon kunne ya sa an ɗage shari’ar ‘Ɗan Sarauniya’ Jin sa ya dauke
Daga Usman abdullahi jibrin
Wata kotu a Kano ta ɗage zaman farko da aka soma a yau bayan an gurfanar da tsohon Kwamishinan Ayyuka na jihar, Mu’azu Magaji.
Lauyan wanda ake zargin ya bayyana cewa an ɗage shari’ar ne sakamakon matsala da kunnen wanda ake zargin yake da shi biyo bayan hatsarin motar da ya yi a Abuja bayan yan sanda sun biyo shi.
Lauyansa, Barrista Garzali Datti Ahmad ya shaida wa BBC cewa sun gaya wa kotu cewa ba za a iya karanta wa wanda ake zargin laifinsa ba sakamakon ba ya ji sosai, ganin cewa a lokacin da ya yi hatsarin, balan-balan ta kariya wadda aka fi sani da “Airbag” ta fito ta daki kunnensa.
Ya bayyana cewa a halin yanzu kotu ta bayar da umarni a mayar da shi asibitin ƴan sanda da ke Bompai a Kano domin a ci gaba da duba lafiyarsa.
-
News4 days agoWasu Ƴan Daba Sun Kai Farmaki Kasuwar Siyar Da Wayoyi Ta Farm Center Dake Kano
-
News6 days agoWasu Fusatattun Matasa Sun Ƙona Mutum Uku Har lahira A Filato
-
News5 days agoAbin Takaici Ne A Kyale Mata Su Cire Wandunan Da Aka Basu Akan Titi Suna Dagawa A Cikin Al’ummar Da Ke Alfahari Da Kunya Da Addini
