News
‘Yan sandan Ogun sun kama Fasto bisa laifin yin lalata da uwa da ‘ya’yan ta
Daga Yasir sani Abdullah
An kama wani Fasto mai suna Timothy Oluwatimilehin bisa zarginsa da kwana da wata mata da ‘ya’yanta mata biyu a Abeokuta, jihar Ogun.
‘Yan sanda sun ce Timothy yana limanci cocin Spirit-Filled International Christian Church a yankin Olumore na jihar.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan, Abimbola Oyeyemi, ya ce kamen ya biyo bayan korafin da mijin da mahaifin wadanda abin ya shafa suka kai ofishin ‘yan sanda na Adatan.
Mijin matar ya ruwaito cewa limamin cocin nasu ya yaudari matarsa da ’ya’yansa mata guda biyu, wanda ya dauke su a hannun sa yana kwana da su.
Bayan kama shi, Timothy ya amsa laifin aikatawa amma ya roki a gafarta masa.
Wanda ake zargin ya ce ya yi amfani da rashin fahimtar juna tsakanin matar da mijinta wajen aiwatar da wannan aika aika.
-
News3 days agoWasu Ƴan Daba Sun Kai Farmaki Kasuwar Siyar Da Wayoyi Ta Farm Center Dake Kano
-
News6 days agoWasu Fusatattun Matasa Sun Ƙona Mutum Uku Har lahira A Filato
-
News5 days agoAbin Takaici Ne A Kyale Mata Su Cire Wandunan Da Aka Basu Akan Titi Suna Dagawa A Cikin Al’ummar Da Ke Alfahari Da Kunya Da Addini
