Connect with us

News

Majalisar Dokoki ta Kano ta sahale gina gidaje 5,000

Published

on

Screenshot 20220201 170955 com.ksmobile.cb2  696x541 1
Daga
Kabiru basiru fulatan
Majalisar Dokokin Jihar Kano ta sahale gina gidaje 5,000 domin ma’aikatan gwamnati da malaman makaranta.
Kakakin Majalisar, Hamisu Ibrahim Chidari ne ya baiyana hakan a jiya Litinin a wata wasiƙa da Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje ya aikewa majalisar don neman ta sahale masa ya aiwatar da aikin gina gidajen a Ƙananan Hukumomi 44 na jihar.
Bayan da Majalisar ta tattauna a kan ƙudurin na gwamnan, da ga ƙarshe sai duka ƴan majalisar su ka amince da aiwatar da aikin ginin.
Da ya ke karanta wasiƙar, Chidari ya ce za a aiwatar da aikin ne a ƙarƙashin jagorancin  Shugaban Hukumar kula da Dokokin Aiyuka da Aiwatarwa ta Jiha, Rabi’u Suleman Bichi.
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending