News
Hisbah ta kwace Barasa miliyan 3 a Kano

Daga Muhammad muhamm zahraddini
Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta lalata sama da kwalaben barasa miliyan 3.8 da aka kwace a watannin baya.
Babban kwamandan hukumar Dr Harun Ibn-Sina ne ya bayyana hakan a yayin lalata giyar da aka kama a Tudun Kalebawa a karamar hukumar Dawakin Tofa ranar Laraba.
Malam Ibn-Sina ya bayyana cewa hukumar na samun nasara a yaki da shaye-shayen miyagun kwayoyi, abubuwan sa maye da duk wasu munanan dabi’u na al’umma.
A jiya ne dai hukumar lafiya ta duniya wato (WHO) ta bayyan Najeriya a matsayin kasar da akafi dirkar barasa a Duniya.