Connect with us

News

KEDCO ta bada haƙuri kan ƙarancin wutar lantarki a Kano, Jigawa da Katsina

Published

on

FB IMG 1644988732770
Spread the love

Daga Muhammad Muhammad zahraddin

 

 

 

Advertisement

Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Kano, KEDCO ya baiwa yankunan da ya ke hulɗa da su haƙuri sakamakon ƙarancin wutar lantarki da a ke fuskanta a ƴan kwanakin nan.

A wata sanarwa da Jami’in Hulɗa da Jama’a na Kamfanin, Ibrahim Sani Shawai ya fitar, ya ce matsalar ta afku ne sakamakon raguwa da kason da a ke baiwa kamfanin da ga cibiyar raba wutar lantarki ta ƙasa.

A cewar Shawai, ita ma cibiyar raba wutar lantarkin ta fuskanci ƙarancin wutar ne sakamakon ƙarancin samar da wutar da ga Kamfanonin da su ke samar da wutar lantarki a ƙasar, waɗanda a ka fi sani da ‘Generation Companies’ zuwa ga KEDCO ɗin da ke baiwa Kano, Jigawa da Katsina wutar lantarki.

Ya ce an fi samun ƙarancin wutar da ga ƙarfe 6 na yamma da kuma 11 na dare.

Advertisement

Bayan da ya baiwa al’umma haƙuri, Shawai ya tabbatar da cewa za a shawo kan lamarin nan ba da daɗewa ba.

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *