Connect with us

News

Jirgin Qatar Airways ya fara sauka a Kano

Published

on

1646232311106
Spread the love

Daga Muhammad Muhammad Zahraddin

Kamfanin zirga-zirgar jiragen sama na Qatar Airways ya fara sauka a birnin Kano da ke arewacin Najeriya a yau Laraba cikin murna da annashuwa daga hukumomin ƙasar da kuma kamfanin.

Jirgin Boeing 787 ya sauka a babban filin jirgi na Mallam Aminu Kano (MAKIA) da misalin ƙarfe 11:00 da ɗoriya.

Advertisement

Jekadan Najeriya a ƙasar Qatar, wadda ta mallaki kamfanin, Ahmadu Yakubu Abdullahi na cikin waɗanda suka halarci bikin saukar jirgin karon farko a tarihi.

Kano ce wuri na uku a Najeriya da kamfanin zai dinga sauka bayan Abuja da Legas. A gobe Alhamis kuma zai ƙarasa birnin Fatakwal na Jihar Rivers a kudancin ƙasar.

Advertisement

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *