Connect with us

News

Ku cigaba da juriya, ai ba mulkin Buhari aka fara rashin man fetur ba: Adesina

Published

on

FB IMG 1646457188761
Spread the love

Daga yasir sani abdullahi

 

 

Advertisement

 

 

Mai magana da yawun shugaban kasa Muhammadu Buhari Mista Femi Adesina , ya bayyana cewa ba mulkin Buhari bane kadai aka fara wahala da tsadar man fetur ba.

Advertisement

Tsawon wata guda yanzu, Najeriya na fuskantar rashi da tsadar man fetur inda mutane ke kwana da motocinsu a gidajen mai.

A jawabin mako-mako da Adesina ya saba, ya bayyana cewa yan Najeriya zasu jure saboda sun jure ire-iren wadannan matsaloli kafin lokacin mulkin Buhari.

“An samu matsalar gurbataccen mai a baya a kasar nan. Mun kwana na tsawon kwanaki da makonni a gidajen mai kuma mun rayu. Wannan ma zamu rayu. Ko ta kaka.”

Advertisement

“Ina kira gareku don tunatar muku da cewa abubuwa basu gurbacewa kasarmu ba.”

“Rashin mai zai so ya tafi. Yan Najeriya kuwa masu godiya zasu ji dadi.”

Kamfanin mai na NNPC ya sha nanatawa cewa, akwai isasshen mai a ƙasar, amma har yanzu mutane suna ci gaba da shan baƙar wahala a gidajen mai, ta hanyar bin dogayen layuka kafin su sha man.

Advertisement

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *